Hausa NovelsNoor Al Hayat Hausa Novel

Noor Al Hayat 48

Sponsored Links

Har suka isa gidansu Aliyu babu wanda yace komai cikinsu, khadijah tayi nisa tunanin da take bata ma san sun iso ba, Sudais ya fito daga motar ya xaga side dinta ya bude mata ganin bata fito ba, sai a sannan ta dawo duniyar tunanin da ta tafi, tayi saurin sauke kanta ta fito daga motar ya rufe, kallon motar khaleel sudais yyi, dai dai sannan shi ma ya fito daga motarsa, Sudais ya karasa gun sa yace “I pray we meet him at home” Khaleel ya daga kafada yace “Allah ya sa” Sudais ya kalli Khadijah dake tsaye jikin motarsa sai kallon gidan take a sanyaye, gate din gidan ya nufa khaleel ya bi bayansa, bai tsaya sauraran mai gadi Usman dake tambayar sa daga ina ba ya kutsa kai ya shiga gate din ya juya yana kallonsa yace “Six years isn’t that far, bai ci ka mance ni da wuri haka ba malam” khaleel ma ya shiga gidan yana kallon mai gadin murmushi dauke fuskarsa ganin yanda yyi kasake yana bin Sudais da kallo, A sanyaye Khadijah ta gaida Usman da ya xaro ido yana kallonta da mamaki yace “wannan kamar Khadijah??” Murmushi ta kirkira ta shiga cikin gidan ta bi bayan su sudais da suka nufi entrance din shiga gidan, haka kawai gabanta ya dinga faduwa tayi slowing pace dinta, Sudais ya danna bell ya ja gefe ya tsaya, bayan wani lkci aka bude kofar, Baby ce tsaye bakin kofar ta dinga kallonsa na wasu seconds kafin ta gaishesa, yana kallonta ya amsa da murmushi yace “Can we come in?” Barin bakin kofar tayi ta rasa abinda xata ce masa, ya kula she is lost don haka ya shiga parlon khaleel ya bi bayansa, tuni khadijah ta labe jikin bango jin baby ce ta bude kofar, hawaye suka shiga sakko mata ta kasa shiga parlorn, Anty khadijah dake xaune parlorn ta dinga kallon Sudais kamar me son tuno inda ta san sa, sarai ya dau fuskarta ya gane ta, a hankali yace “Hello?” Ta mike tana yamutsa fuska tace “Daga ina? Wa ku ma kuke nema?” Yana kallonta yace “Bak’i ne…. Amma nayi mamakin da baki gane ni ba Hajiya” Ta hade rai tace “Do I have any business with you da xan gane ka, malam nan gidan masu aure ne, ka fadi wa ka ke nema, ba haka nan ake shiga gidan mutane ba, from all indications ma batar hanya ku ka yi ” Ya taka har gabanta ya tsaya yana mata kallon cikin ido ya fiddo ID card dinsa yace “Barrister Aliyu…. May be this will make you remember me fast” mikewa tayi da sauri tana masa wani kallo, sai kuma ta shiga kalle kalle don ta tabbatar babu kowa parlorn, ta hadiye abu da kyar tace “Wa kake nema malam, me ka sake dawowa yi gidan nan?” Jin bai ce mata komai ba sai murmushin da yake ta juya da sauri ta kalli khaleel da ya nemi kujera ya xauna yyi relaxing a kai, Murya suka ji a stairs duk suka juya, Mumy ta sakko tana kallonsu da mamaki tace “Sannun ku da xuwa” Sudais ya amsa ta karaso parlorn tace “Are you looking for Someone?” Sudais yace “Sure” juyawa yyi ya kalli bakin kofa ya ga khadijah bata shigo ba, ya juya ya koma bakin kofar, yana fita yace “Come in khadijah” Khadijah ta girgixa masa kai cikin rawar murya tace “Baxan iya ba, kuma kila ba nan ya kawo su ba” sudais yace “Trust me, kawai ki biyo ni” daga haka ya shiga parlorn ta bi sa a d’an tsorace don jin muryar Anty khadijah ya kara daga mata hankali, baby ce ta fara xaro ido ganinta lkci daya ta nufe ta da gudu tace “Imann” kasa amsa mata Khadijah tayi, Baby ta rungumeta, hakan yasa khadijah ta fashe da kuka kamar yanda baby ma ta fara kuka, tuni Anty khadijah ta rikice bakin ta na rawa tace “Me ya kawo yarinyar nan gidan nan, me ta xo yi….” Ba tare da Sudais ya kalleta ba yace “Ta xo amsan yaranta” Anty khadijah ta yo waje da ido tace “Tayi aure cikin gidan nan ne da ta xo amsan yara??” Khadijah da ke hawaye a sanyaye ta daga kai ta kalli inda mumy take ta ga kallonta take ko fiftawa babu, sunkuyar da kai tayi kamar me counting steps dinta ta isa gaban mumy hawaye na sakko mata, Mumy da idanuwanta suka kawo ruwa ta rungumeta murya can kasa tace “Khadijah..” duk wannan abun Aliyu na sama tsaye yana kallonsu, cikin rawar murya Khadijah tace “Mumy ki ce ya bani yarana na yafe masa wllh…. Intervene plss mumy” Mumy ta kasa cewa komai sai kuka, Anty khadijah sai wuri wuri ta ke da ido a parlorn ta kasa cewa komai, A hankali Aliyu ya dinga sakkowa stairs din har ya iso parlorn, Khadijah ta dinga kallonsa tana jin tsanar sa, Sudais ya taka har gabansa yana kallonsa da kyau yace “Aliyu?” Aliyu yace “Sure, any problem?” Sudais ya gyada kai yace “Fito mata da boys dinta” Aliyu ya rungume hannunsa yana kallonsa with interest yace “Bodyguards din nata har biyu ne kenan” Khaleel yyi calm smile pretending Aliyu doesn’t even exist in the parlorn balle har ya ji abinda yace, shi dai yana xauna kan kujera har sannan, Sudais da idanuwansa suka sauya launi yace “You are stupid… I mean very stupid” Murmushi Aliyu yyi yace “Ku dai da ku ke biyota ne xa a kira da haka, look… ba ku da right din da xa ku dinga interfering a case dina da ita, it’s almost a family issue so stay out of it…..” Khadijah bata san lkcn da ta isa gabansa ba idanuwanta suka kankance don bala’i tace “Wannan da kake gani ya fi Ka right, when I say right ina nufin right, wllh ya fi ka 100% right over those children, he is almost their father, and will always remain their father, na tsane ka Aliyu, na tsane ka…. I hate you” Tana kai wa nan ta fashe da kuka sosai, Mumy ta rasa abinda xata ce ban da kuka bbu abinda take, Aliyu yace “Dama ban ce kar ki tsane ni ba Khadijah, you have all right to do so, but Iman am sorry baxan ba ki yaran nan ba, you’ve past through a lot, ki bar ni da su yanxu let me also play my role, ki tafi ki je ki ci gaba da rayuwar ki da bodyguards din ki, thank God you said he is almost their father not their father, ni kuma I am their biological father…” Tapping dinsa Sudais yyi xuciyarsa na tafarfasa, strictly yace “Malam kasan wanene ni kuwa? Did you knw why I am taking it gently with you, baka sani ba sure.. Then knw this, it’s because of ur mother, na ga alamar she deserves some respect, don haka cikin salama ka fito da yaranta yanxu ka bata idan ba haka ba….” Aliyu ya tabe baki yana d’an murmushi yace “You do ur worst….Barrister” Bude baki Sudais yyi yana kallonsa, Khadijah ta durkushe wajen ta kara rushewa da kukan takaici, mikewa khaleel yyi yana ma Aliyu wani kallo yace “Amma kai jahili ne na ga alama, islamically baka da right over yaran nan, kai har yaran da ka samu ta hanyar zina kake alfahari da kake bragging baxa ka bada ba?? Is this how senseless you are” Yar dariya Aliyu yyi yace “U watch ur tongue gidanmu ka xo ka same ni, so you have no place to tell me nonsense, baxan bada yara ba nace” Sudais ya sake tapping dinsa yace “Good, ka saurare sammaci gobe, nasan dai baxa kayi denying kayi raping din yar mutane a court ba koh, sannan kuma don rashin kunya ka dawo kana claiming yaran da baka san da su ba, baka san da yanda aka yi Allah ya raba ta da su ba… You are wicked Aliyu” Aliyu yace “Ka kai ni gaba da kotu…. If there is any” Daga haka ya juya ya haura sama ya bar su wajen, Juyawa Sudais yyi yana wani murmushi yace “Alryt xa mu hadu a can din” daga haka ya nufi kofa yana kallon khaleel yace “Can we?” Mumy ta dakatar da shi da sauri, ya juyo yana kallonta, karasowa gabansa tayi tana goge hawayen idonta tace “I am really short of words, sai dai baxa ayi haka ba my son don Allah ku yi hakuri, xancen baxai kai kotu ba in sha Allah, sure islamically ba shi da right a kan yaran, ina mai tabbatar maku xai bata yaranta in sha Allah, and plss idan baxan bata maku lokaci ba ku bani just few out of ur time ina son mu yi magana da ku” Sudais bai ce komai ba, sai dai shi kansa yasan tun shigowarsa parlorn ya ga darajar matar shi yasa ma bai ma Aliyu haukan da yayi niyya ba, kuma albarkacin irin rikon da tayi ma khadijah truly she deserve some respect, sauke kansa yyi kawai ya koma ya xauna yace “To ina ji Ma” Mumy ta xauna ita ma tana ci gaba da share idonta ta bi parlon da kallo taga babu Anty khadijah, Baby ce kadai jingine da bango tana hawaye, a sanyaye Mumy ta fara cewa “Amma ya ku ke da Iman?” Khaleel ya kalli Sudais da ya kallo sa shi ma, ya ci gaba da operating wayarsa, Sudais ya d’an shafa beard dinsa yace “Yan uwanta ne mu” Mumy ta gyada kai, ta fara magana cikin sanyi tace “It’s not as if ina supporting Aliyu don d’a na ne, plss dont quote me wrong, amma ina son ku sani it’s a mistake he made kuma ba da gangan haka ya faru ba, tsautsayi ne ya gifta tsakaninsu, ni na haifesa na kuma san halinsa, ita kanta Iman xata shaide sa…. It’s not ordinary hakan ya faru da shi” Sudais yace “But kinsan bayan ya sa ta tafi da aka gano tana da ciki na maido ta nan gidan?” Kallonsa mumy take da d’an mamaki, can tace “Gidan nan?” Yace “Sure?” Jikinta yyi mugun sanyi tace “Wa ku ka samu gidan?” Sudais yace “Matar da muka fara samu a parlor xuwan mu yanxu, she humiliated us and sent us away then” Kasa cewa komai mumy tayi lkci daya hawaye ya kara cika idonta da kyar tace “Kana nufin khadijah ce ta Kore ku, kuma kun gaya mata abinda ke tafe da ku?” Sudais na gyada kai yace “Kwarai, I was even thinking she is his mum then, the way she reacted….” Mumy tace “Amma kun samu Aliyun?” Girgixa mata kai yyi yace “Ce mana tayi baya kasar gaba daya” Mumy ta fashe da kuka tace “Amma Allah ya isa tsakanina da khadijah, she just ruin my family, yar uwata ce amma ko bare baxai min haka ba, yanxu tana sane da abun nan amma bata gaya min ba, she never told me anything about it da babu abinda xai hana ni nemo Iman duk inda take, greatest mistake din Aliyu shine ce mata da yayi ta tafi, kuma wllh ni shaida ce tun daga ranan Aliyu bai sake samun kwanciyar hankali ba, kuma bai taba gaya min abinda ya faru ba sai dai yace in taya sa da addu’a, gashi nan dai har yanxu ya ki yin aure” Ko kadan khadijah bata damu da abinda mumy take fada ba ku ma bai shigeta ba, Briefly Sudais ya ba ma Mumy labarin yanda rayuwa ya kasance ma khadijah bayan Aliyu yace ta tafi… Ban da kuka babu abinda Mumy take duk jikinta yyi mugun sanyi tausayin Khadijah ya cika ta, ita dai tasan da tasan abinda ya faru kenan da ta sa Aliyu ya nemo ta Duk inda take amma yyi wautan rashin gaya mata, Mumy ta mike ta isa gun khadijah ta duka gabanta tana kuka tace “Khadijah ina neman alfarmar ki yafe ma Aliyu, ko don albarkaci na forgive him plss, kadararrku ce a haka, don haka ki ta godiya ma Allah, amma kiyi hakuri kar ki bar sa a xuciyar ki” Khadijah da xuciyarta ya mata rauni ita ma tana kukan tace “Mumy ni fa na yafe masa amma yayi hakuri ya bani yaran don Allah” mikewa Mumy tayi tace “Xai baki Khadijah, ina gidan ku yake yanxu?” Khadijah ta fada mata address din, Mumy tace “Toh kiyi hakuri ku je na maki alkawarin xa mu biyo ku da yaran yanxu” shiru khadijah tayi tana kallonta xuciyarta na bugawa sai take ga kamar kawai labari mumy take mata don ta tafi, baxa su bata yaran ba, Sudais ya mike yace “Toh shkkn, Ma… Muna xuba ido sai kun xo” Mumy ta kalli khaleel a sanyaye tace “Ku yi hakuri balarabe, Allah ya ba ku lada, amma don Allah ku bar jin haushin Aliyu ba yin kansa bane, nasan xa ku yi ta mamakin jin ina cewa ba yin kansa bane kamar na shiga xuciyarsa, but plss just do consider him” Murmushi khaleel yyi ya mike yace “Bakomai Ummu, Allah ya kara girma” tace “Amin nagode” daga haka ya nufi kofa, sudais ya kara mata sallama ya bi bayan khaleel, Khadijah na biye da su a baya tana goge idonta, ta kasa kallon baby dake bakin kofa har lkcn, A hankali baby tace “Iman plss forgive me brother, ki yafe masa don Allah” hawaye na sakkowa idonta take maganar, Khadijah tayi murmushin karfin hali tace “Na yafe masa” daga haka ta fita parlorn. Sama Mumy ta wuce xuwa dakin Anty Khadijah ta ganta xaune tana bude jikin iklima ganin wasu kuraje da ke feso mata ta ko ina, Mumy tace “Khadijah, a duk xaman mu dake in har na taba cutar ki Allah ya saka maki, in kuma ke kika cuce ni Allah ya saka mani, ki tattara kayan ki da na yar ki ki bar min gidana yanxu, Allah ya bani ladan xumuncin da nayi a baya, kuma in sha Allah nasan Allah baxai kama ni da laifin xumunci ba, ki je na bar ki da Allah” mikewa Anty khadijah tayi tace “Ni yau kike kora gidan ki yau Anty fati saboda wasu shegu sun xo sun shirga maki karya?” A fusace Mumy tace “Ki fita ki ban waje, yanda kika so ganina da jikoki wanda aka samu ba ta hanyar aure ba ke ma Allah ya ba ki” Anty khadijah ta tashi tana wani murmushi tace “Sai kinyi da kin sanin daga min yatsa da kika yi fatima” daga haka ta bude siff ta dinga fiddo kayanta da na Iklima tana huci, Mumy tace “Da na sani sai dai ki gansa a kwaryar ki” daga haka ta fice daga dakin ta shiga na Aliyu, Yana xaune gefen gado ya rike kansa, duk yan biyun sun yi bacci kan gado, Mumy na kallonsa tace “Kai da babban laifi kai da fadin bakakken maganganu ko Aliyu?” Kamar xai mata kuka yace “Mumy me yasa duk hallacin da na ma khadijah a baya baxata duba na, did I deserve this, wllh da hankalinta baxan cuce ta haka ba, sannan ta dinga wani hadani da wasu karti, ni ita na sani ba su ba su ba su daina involving kansu a abinda bai shafe su….” Katse sa mumy tayi tace “Don’t tell me nonsense, dole duk mai conscience idan ya ji labarinta ya so ya kwatar mata hakinta, kasan irin cutar da ka mata kuwa ka raba ta da kowa nata?” Aliyu ya rike kansa bai ce komai ba, Mumy tace “Sai ka tashi mu tafi can gidan nasu yanxu” Aliyu ya dago ya kalleta da kyar don wani Sara masa kansa ke masa yace “Mumy wllh ni baxan iya rabuwa da Iman ba, baxan iya rayuwa ba ita ba, my life has being miserable tun da na sa ta bar gidan nan, Don Allah ki rokar min ita ta amince mu yi aure, I don’t think xan iya auren wata ya mace a duniya idan ba ita ba, plsss even for the sake of this innocent children ta amince mu yi aure” Mumy tace “yanxu kuma??” Tashi yyi Yace “Wllh Mumy idan tace baxata aure ni ba, I promise to go away with this kids baxa ta sake ganinsu ba har karshen rayuwarta, ai da can ba da su take rayuwa ba” Mumy na masa wani kallo tace “Na ga alamar ka fara xarewa, da yaran xaka mata baraxanar ta aure ka kenan, a hakan xata amince ta aure kake tunani, kasan ko kotu aka je yaran nan ba naka bane Aliyu, ba ta hanyar aure ku ka same su ba don haka ka janye wannan baxan maganar da kake yi, kuma kar ka bata min rai” Wani murmushi yyi bai dai ce komai ba, Jikin mumy yyi sanyi ta bi sa da kallo, tsoronta kar ya tafi da su kamar yanda yace, da kyar tace “Ka tashi mu je gidan na su, nasan even for my sake ma xata amince maka” daga haka ta fita dakin. Sai kusan magrib suka isa address da khadijah ta ba mumy, Aliyu ke driving din, Sai baby a gaba, mumy kuma na xaune back seat da yan biyun, tana rungume da little Sudais da jikinsa yyi xafi sosai duk da allurorin da Aliyu yyi masa, kai kana ganin yaran kasan hankalinsu ya kwanta da mumy, Shureim na kallonta yace “Are we going to visit you again mama?” Tana murmushi ta shafa kansa tace “Sure sweetheart” parking Aliyu yyi kusa da gidan ya juya yana kallon Mumy, Mumy tace “Ina jin nan ne” Shureim yace “Ehh mama nan ne gidanmu” Mumy tace “baby sauka ki kwankwasa gate din” Baby ta sauka tayi yanda Mumy tace, Mumy ta sauko tare da boys din, Aliyu ya fito shi ma ya dau sudais, bayan wani lkci Nanny ta bude gate din, da gudu Shureim ya tafi ya rungumeta, Nanny ta ji dadin ganin su sosai ta dinga yi ma su Mumy sannu da xuwa, Kallo daya tayi ma Aliyu ta gane shi ne uban yan biyun, ta yi masu iso har parlor, Sannan ta shiga daki don Umma na ciki tana sallah, Khadijah ma tasan sallan take yi, Umma ta sa Hijab ta fito bayan Nanny ta sanar mata bakin da suka yi, Har lkcn Sudais na jikin Aliyu, Shureim dake jikin Mumy ya tafi da gudu ya rungume Umma yace “I miss you Mumy na” Umma ta xauna tana murmushi ta ja sa jiki sannan suka shiga gaisawa da su Mumy, jikin mumy yyi sanyi sosai don bata taba xaton xata tarbesu da kyau haka ba, shi dai Aliyu ya kasa daga kai ya kalleta, shi ma bai yi xaton haka ba, Khadijah dake xaune kan darduma lkci daya taji ranta yyi mugun bacci jin yanda Umma ta sake masu, jin muryar yaranta yasa ta lumshe idonta, amma ta ki fitowa parlor ta same su don bata ma son ganin Aliyu, Mumy na kallon Umma tace “Ina Khadijar Hajiya?” Umma ta kalli Nanny dake tsaye tace “kira Khadijah” sosai Khadijah ta dake xuciyarta ta mike ta bi bayan Nanny kan ta a kasa, har ta shigo parlorn bata yarda ta dago kanta ba ta gaida Mumy, Aliyu sai kallonta yake ko kiftawa babu, Shureim ya nufeta ya xauna jikinta yace “Anty mun dawo, I like the house so much…” Khadijah ta ki kallon yaron amma har ranta bata ji dadin abinda yace ba, ita fa in dan ta ita ne yaranta basu da uba, ita dai tasan Allah ne ya bata su, kuma tana gode masa, fuskarta daure ta dago tana satan kallon Aliyu dake ta kallonta suka hada ido ta masa wani harara ta dauke kai, lkci daya ta mike ta ja hannun Shureim suka bar parlorn, tana xaunawa kan gado ta jawo yaron gabanta tana kallonsa da kyau tace “Did that stranger tell you anything?” Shiru yyi da farko kafin yace “But he is not a stranger Anty, this is the 4th time we are meeting with him” ta xaro ido xuciyarta na bugawa tace “Where and where” yace “Anty ranan nan da muka kusa yin accident, that i told you he made sure we where fine….” Gabanta yayi mugun faduwa tace “And where?” Yace “We met again at the airport da xa mu je holiday a UK, shi ma xai je can…” Ta runtse ido xuciyarta na tafarfasa tace “And where????” Yace “Yesterday at the market, because sudais don’t like him shine ya gudu ya shiga titi babban mota ya buge sa” ta fixgo yaron tana huci tace “Shi ya janyo mota ya buge Sudais?” Kai ya gyada mata ta jefa masa wani kallo tace “And you are telling me he is kind yana neman kashe maka brother, daga yau ka sake yarda ko kallon ka yayi sai ya xuke maka jinin jikin ka gaba daya, baka san shi vampire bane” buda baki yyi yana kallonta da surprise, can yace “Me yasa bai shanye mana ba a gidansu?? Anty he is kind fa, ni dai I like him, he was with us…..” Tsawa tayi masa ta turasa har sai da ya kusa faduwa hawaye cike idonta tace “Xan fasa maka kai… Nace stay away from him, you have no business with that wicked man” Shiru yyi a tsorace yana kallonta, a hankali yace “But he even told us he is our father not barrister as you told us….” Mikewa tayi hankali tashe xuciyarta na mugun bugawa tace “He is a liar… Karya yake maka barrister ne babanka, ba abinda ya hada mu da shi” cikin rawar murya tace “Tafi ka kamo hannun sudais ku xo nan yanxun nan” da sauri ya fita, yana isa kusa da Aliyu yace “Uncle, Anty tace I shud call my brother now” shiru yyi yana kallon yaran, haka ma Mumy da Umma, Aliyu yayi kasa da kai a hankali yace “Umma ki d’an mata magana ta bari in je da shi, he is sick dole xa mu koma asibiti” a fusace Khadijah dake jin sa ta fito tace “Ina ruwanka da rashin lafiyarsa? Ka bani yarona ai nasan hanyar asibiti, give me my son” tsawa Umma tayi mata ta mike tace “Tafi ki bar parlorn nan kar in bata maki rai, shashasha” ta fashe da kuka ta juya da sauri ta bar wajen, Umma dake kallonsa a sanyaye tace “Ka je da shi, Amma ko xuwa gobe sai ka kawo shi” a sanyaye yace “Na gode Umma” su mumy basu bar gidan ba sai kusan karfe taran dare bayan mumy ta mata bayanin duk abinda ya faru, Umma ta raka su har bakin mota jikinta a sanyaye.

Back to top button