Hausa NovelsMatar Makaho Hausa Novel

Matar Makaho 18-19

Sponsored Links

Page1️⃣8️⃣&1️⃣9️⃣
Washhhh yace jinsa a k’asan cafet ya zube,Bai farga ba Yana kokarin mikewa, yaji ta Fad’i a kansa daga shi har ita Kara suka saka sai Kuma sukayi shuru tare,

ido na ware jina a jikinsa cikin rawan jiki duk na rikice na fara chuku chukun mikewa naji yasa hannu ya zagaye hips ina,
sosai ya kara matsota kusa dashi,

“Kai me haka” ? Ka sakeni Mana, Mena rike min……..sai Kuma tayi shuru ta kasa karasawa,

Cikin sanyin halinsa ga jikinsa na wani irin rawa Jin mace a jikinsa a karon farko a tarihin rayuwar sa kenan, yaji mace a kwance a jikinsa, Mena rike Miki? Ya tambaye ta Yana yawo da fuskarsa a kafadar ta Yana neman fuskarta, so yake ya Hada fuskar ta da tasa,

“Wai ma Ina ruwanka ne don Allah nikam sakeni haii” nace cikin ihu

Jin muryarta hakan ya tabbatar Masa da inda saitin fuskarta yake hada fuskar yayi da tasa har suna Jin numfashin juna,

“Wai menene haka bazaka sak”………bai bare na karasaba naji saukan lips nashi masu uban dume akan nawa lips in wani abu naji ya tsargar Mini daga tsakar kaina har farcen kafana cikin wani irin birkita na yunkura zanbar jikinsa zan mike ji kawai tayi ya fisgoni gabaki d’ayana na zube Akansa ,
cikin wani irin zafin nama da kuzari ya cafke lallausan bakinta cikin nasa da wani irin zafi zafi yake tsotsarta Jin sai k’okarin mikewa take a jikinsa yasa kafa ya harde kafarta da nasa kafar,daga ita harshe rawa jikinsu yake,

Tashin hankali da nake ciki ba’a saka Masa Rana kuka nake so nayi Amma ba Hali hawayene kawai kebin kumatuna,

Jin saukar hawayenta akan face nasa ya saka sa sassauta Mata riko a hankali ya zame bakinsa cikin nata,

Ai da wani irin azabebben sauri na mike tsalle D’aya nayi na fita a d’akin na tsaya a baranda duk sanyi da ake da ruwanda ake zugawa na g’wammaci na kwana a waje Data kwana a d’akin nan inaaaaa,

Sumayya!!! Sumayya!!! yake kiranta cikin tsarkewar murya shima ya mike Yana lalube ya fitoh wajen,

ganinsa ya sakani zabura Amma tunawa da nayi baya gani yasa na tsaya naki Koh motse kirki Ina jinsa sai kirana yake Yana lulube na a baranda in yazo lalubar Gefen da nake saina matsa a hankali na koma inda ya laluba,jikina nata rawa,

Jin baijita ba don karfin ruwanda ake Bai bare yaji Koh D’an motsen taba don ruwa ake harda tsawa,sauka yayi a baranda yanakan lalube,
ruwa na dukansa Yana zaga kofar Amma Bai jita ba har kofar shashen ya taba Jin kofar a rufe yasa ya gane Bata fita a kofar ba,

Don Allah Sumayya ki kulani Koh zanji hankali na ya kwanta don nasan kina jina kina ganina,

Wani irin tausayin sa naji ya kamani ,cikin sanyin jiki da fargaba nace “ganinan anan,”

Ai da hanzarinsa ya nufi barandan jikinsa ya jike jakaf da ruwa haryana diga ga gashin kansa da gemunsa duk ya jike ya k’wanta g’wanin sha’awa ,

Da hanzari ya iso wajen ta cikin rawan murya ya fara magana, Sumayya pls mu koma d’aki kinji,

“Nidai yau bazan k’wana da kaiba a d’aki D’aya ba “nace Ina kuka Kamar karaman yarinya,

Kiye hakuri kinji Sumayya muje mu k’wanta Allah bazan miki kome ba kinji Koh,

“Wallahih nidai bazan shigaba” Ina fada Ina kuka, ganin Yana matsowa kusa Dani yasa na k’wala Kara Zan ruga cikin ruwa naji anyi sama Dani,

D’aukarta yayi duk yanda take kuke kukenta kin kulata yayi sai ihu take tana ya sauke ta, sosai ya riketa Gam a kirjinsa Yana lalube har suka shiga dakin ya tura kofar da hannunsa d’aya d’ayan na rike da ita ,

A hankali yake lalube harya Iso bakin gado a hankali ya haura saman gadon kwantar da ita yayi a hankali ya lalube blanket inta ya rufa Mata ,ya sauka Akan gadon cikin lalube ya shiga neman Ghana must go in kayansa wani jallabiyan ya dauka a wanke tas ya zura ya zame jikekken gajeren wandon sa,
lalube yayi ya fita waje a aje a cikin kayansa jikakko daya aje a boket,

Nikam tunda ya saukeni a Kan gadon jikina yake ta rawa sosai naji wani irin tsoron Daren nan, zazzabinane ya Tashi sosai nakejin kaina na Sara mini yau tension Yama kaina yawa,

Dawowa yayi Kan kujira zai k’wanta Amma yaji baho a saitin wajen, lalubawa yayi yaji kujiran a jike hakan ya tabbatar Masa lalai yo-yo wajin ya ke filon kujiran da yake k’wanciya dashi ya dauka ya lalube cafet ya aje ya k’wanta a kasan dakin wani irin sanyi ne ke shigar sa don a lokacin baiki ya samu abin rufuwa ba Amma Bai dashi Kuma baida karfin gwuwar tambayar Sumayya tunda ba ita tayi niyar basa ba,

Jin motsen yayan Khadija yaki natsuwa sai jujuyawa yake ga atishawa akai akai alamudai murace ta kamasa,

Wayarda na wancakalar dashi na dauka na haska inda nakejin motsen sa ganinsa nayi a kwance sai jujuyawa yake alamudai sanyi yakeji,

D’an tausayi ya bani sai Kuma na tuna lokacin da bani da lfy dashi da Yar uwarsa su sukayita d’awainiya Dani Amma yau shine na Bare a kwance a kasa ga sanyi,
ni Ina kwance a gado da bargo,

Kamar bazanyi magana ba a hankali nace “,kazo ka kwanta a gadon kasan nan akwai sanyi Kuma naji Kamar mura nason kamaka”

A hankali ya mike ya Soma lalube harya Iso bakin gadon cikin nutsuwa ya haura dai dai ta bakin ya kwanta,

Nikam Ina karshen gado ta wajen jikin gini ganin Bai taba blanket in ba bare ya rufa, yasa na mike na dauko wani a whdrp na aje Masa a kansa na wuce filina na kwanta addu’ar bacci nayi na shafa na juya masa baya ,

Jin ta aje Masa blanket yasa she d’auka ya lulluba shima addu’ar bacci yayi ya lumshe idonsa Sam yaji bacci ya kaurace Masa wani irin yanayi yau ya tsinci kansa a ciki,Mai ban Al’ajabi

Daga shi harni Babu Wanda ya rintsa har 1:00 na dare kafun bacci ya dauke ni shikam bansan lokacin da yayi bacci ba,

*********
Yaukam dagani harshe sai kusan 6 mukayi sallan asuba a dadafe dukan mu biyu da ciwo Muka kwana ga yunwa don tun karyawan safe dagani harshe bamu sake saka kome a bakin mu ba,

muna idarwa gado Muka koma muka sake k’wanciya don baccine ya cika Mana ido na rashin Yi da wure jiya,
Jin Yana matsowa kusa Dani yasani matsawa da sauri ji kawai nayi ya mike zaune ya zura hannunsa ta saitin da nake ya jawoni duka jikinsa a hankali ya koma ya kwanta Dani a jikinsa ,

Yanzun Kam ban neme k’wace jikina ba saboda zazzabinda nake fama dashi ma ya isheni,

A hankali nace Masa”Wai meke damunka ne tun jiya kake ta tabani”?

Nima ban sani ba haka kawai nakejin inason kusanci dake,ya fada da muryarsa da ta dishe don mura kamasa Tay sosai ga fuska jazur kamar ka taba jini ya zuba,

Kala bance Masa ba don ni jikina ne ya dameni,shuru mukaye gabaki d’ayan mu har bacci ya dauke mu a haka,

sallama nake ji kamar muryar Khadija sama sama cikin bacci sai Kuma naji yayan Khadija na zame jikinsa a nawa,

Bude ido nayi Wanda nakejin nauyinsa sosai ga xaxxabi,

Khadija Kam ganin takalmin Aunty da na yayanta a bakin dakali yasa ta juya zata fita Amma dai tana mamakin har 10:10 na safe yayan ta Bai fita ba,

Mikewa Al’ameen yayi ya fita a d’akin Jin alamun Mai sallamar na kokarin fita a shashen Kuma ya shaide muryar Khadija ne,

Waalaikumu salam Khadija ya kina komawa kuma?

La Yaya Daman nace bara nazo na duba Aunty jiya kafarta tun a hanya ya kumbura Amma dai ba kome anjima Zan dawo,

Saboda me?

Naga baku tashi ba Yaya,

Ah ah ai gwarama da kikazo Nima Yanzun nakeson fita na nemi yaro ya kiramin ke,

Lafiya Kam Koh? Naga fuskarka ta kumbura tayi ja ga murya a dishe Daman Saida na tuna haka wallahih ruwan jiyan nan ya kare a kanka,

Ai bani kadai bane Khadija Aunty kima ba lfy ,

Subhanallah meke damunta Hala kafar ke ciwo,?

Ah ah Khadija zazzabine,
Meya faru da kafartan ne da kike ta cewa Yana ciwo,?

Ba kome kasan jiya bamu samu Keke da wure ba Koh?da kafa Muka ringa takawa,

Uhmm lallai fa,yace Yana dafe kansa dake Sara Masa,

Sannu yaya kanne?

Wallahih Khadija,

Toh kaje ka kwanta Mana bara na gyara kofar,

Khadija Aunty ki tun karyawan jiya bataci kome ba zoki karbi D’arin nan ki sai Madara 50 da bornvite 50 akwai sugar n jiya da safiya da Lipton ki hada Mata tie Koh zata iyya Sha?

Toh Yaya Kaifa,

Khadija hada Mata kawai taima kayan shayen bazai Isa ba?

Zai Isa Yaya,

Toh shikinan ki hada hardani

Toh

D’akin ya shiga yadau kudin ya mikowa Khadija ya dawo ya kwanta, tare da matsowa kusa dani

Nidai Ina jinsu shuru kawai nayi,

10:30 Khadija ta dafa Mana shaye harda k’wai ta soya dayake jiya yasai kayan Miya na dare yazo ya samu bamu dawo ba,

Tana Gama shirya kayan Karin ta nufi dakin,

A bakin kofa ta tsaya tana sallama Bata shigo ba ,

Mikewa yayi ya zauna a bakin gadon ya sauke fararen kafarsa a kasan cafet,amsa Mata yayi hade da Bata izzinin ta shigo, Khadija ki shigo mana,yace Jin Taki shiga,

Da sallama a bakinta ta shigo d’akin aje kayan hannunta tayi akan cafet,zata juya,

Khadija d’auki baf in Kan kujiran nan kikai waje kizo ki jona fanka naji Kamar an kawo NEPA ki juyashi saitin kujiran samun ya bushe,

Toh Yaya tace tana daukan baf in tayi waje dashi zubar da ruwan tayi ,

Ta dauki tsintsiya ta shigo dakin tire in kayan karyawan ta dauka ta daura akan kujiran ta share dakin,
fanka ta kunna ta matso dashi Kusa da kujiran,Kamar yanda yace

Turarukan UMSAD INCENSE da ta Gani a jere akan mirror ta d’auka na d’aki jona kaskun lantarki tayi Aiko take dakin ya dauki kamshi Mai Dadi (kowa yasan yanda Turaren wuta yake da kamshi a d’aki especially a damuna),

Khadija na fita ya matsoni a hankali hannu yasa Yana laluba ta nikam sai matsawa nake duk inda naga hannunsa zai taba saina matsa agun,.

Don Allah Sumayya ki tsaya Mana kaina ciwo yake wallahih Koh motsasa bana sonyi kina ta bani wahala yace Yana dafe Kan,

Toh ni sai ka min magana da hannune bazaka mini da baki ba saikayita tabani,

Sorry tashi kije ki wanke bakinki ga breakfast Khadija ta hada Mana yace Yana kwanciya,

Toh Kaifa bazaka wanke bakin bane kake k’wanciya sai yayi ware? nace Masa Babu alamar Wasa,

Murmushi yayi har fararen hakoransa masu tsananin kyau suka bayyana,ai kinfi kowa sanin bakina nada ware Koh babu tunda kin d’and’ana jiya , ya fada muryarsa a shake

Ohon maka dai nace cikin Jin haushi mikewa nayi a hankali na nufi kofa shima mikewar yayi yabi bayana ,

Kofata nabi da kallo tasss Khadija ta share samunta ma nayi tana wanke wanke ga kayan na data cicire a igiya ta zuba a boket,

Khadija kibar d’aurayan nan don Allah daga kin wanke Kwanukan nan ya Isa haka ke baki gajiya da aikine,

Toh aunty tace mini,

Wanke baki mukayi muka koma daki abincin na jawo Mana ganin hadamu tayi plate d’aya tie ne kawai kowa da cup nashi,

,k’wala Mata Kira nayi”Khadija Khadija”

Na’am Aunty ganinan zuwa,, tace
Tana shigowa dakin

“Jiki d’auko wani cup da plate”toh tace ta fita sai gata ta dawo dasu

Ajjyemin tayi zata fita,

“Tsaya Khadija” nace zuba Mata tie nayi na ibi k’wai data soya Mana NASA Mata a plate itama” d’auka kije kici nasan dafawa kikayi baki ibi naki ba Khadija kullum Ina gayamiki in kin girka Abu ki ringa zuba rabonki kinji Koh kin manta nan ma gidanku ne”?

Toh Aunty tace tana karban plate da cup in tayi waje,

Bismillah na Masa ya matso yasa hannu kad’an naci,naji ya isheni don bakina ba Dadi sam tie kawai nashanye duka, Koh aje cup banyi ba wani irin amai ya tasar mini da gudu na fita waje na ringa shika Amain sosai,

Mikewa yayi yabi bayana daga shi har Khadija sai sannu sake mini Mika min ruwa tayi na wanke bakina na koma d’aki
duk k’wanciya Muka sake don shima bazai iyya fita wajen sana’a ba,

Misalin karfe d’aya na Rana ana kiraye kirayen sallah azahar ya mike ya fita, wanka yayi a dadafe ya nufi waje zaije chemist in jambusko Koh zai basa bashin magani Koh iyya Sumayya kawai ma in zai samu a Bata ya gode Allah duk da yasan halin inyamurin daker ya ya basa bashi,

Yana fita Nima mikewa nayi Ina Jin jiri jiri na fitoh waje Jin ana kiraye kirayen sallah Khadija na samu ta wanke Mana kayan mu daya jike jiya,tana kitchen wani aikin Kuma take,

“Khadija Wai me yasa bakiji ne nace Miki kibar aikin haka ”

“Ke kullum kikazo guna baki abinyi sai aiki”

Toh Aunty in ban Miki ba wazan ma ba lfy bane dake ga kofa kasha kasha Koh abincin da zakuci bazaki iyya girkawa ba toh Aunty in ban muku ba wazai muku

A gaskiya bansan dame Zan sakawa Khadija ba Allah ne kawai xai biyata

Nagode Khadija Allah ya barmu tare ya nuna mini auren ki in ban mutuba,hhhhhh nace Ina dariya

Kai Aunty tace tana rufe fuska Wai kunya,

Yana fita gida massalaci ya shiga ana idar da Sallah yanufi chemist in jambusko,

Yana Isa sanin ba musulmi bane yasa ya ce Masa , excuse,?

Yes wanene?

Nine jambusko,ya basa amsa Dayake inyamurin ya Dad’e a Jala yanajin hausa sosai ,

Wai MAKAHO Kaine anan yau kuma?

Eh wallahih madam ce ba lfy zazzabi ke damunta……..

Bai bare ya karasa bama ya ce kaima ai harda Kai bakaga muryarka ba ga fuska yayi ja ido ya kumbura,kana mura,

Eh harda ciwon kaima shiyasa nazo wajen ka ka taimaka kaban bashi inna d’an ji sauki zuwa anjima zanfito in Allah yasa na samu kasuwa saina biyaka, ya fada cikin zullumi don shi kansa Allah ya gani kwata kwata bayason roko Koh bashi Amma ya zaiyi bazai iyya zuba ido Yar mutane ba lfy ya barta haka na shi Karan kansa Saida lfyr zai nema musu abinci

Heeeee chinekeeeee gaskiya MAKAHO nii………..

*Gaisuwa na musamman gareki ummee zariya Naga special comments naki Kuma Nima na yaba Miki sosai naji dadi* 🍀🍀🍀🍀🍀

🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀 *Albishirin ku Mata ku marmaso kuji sirrin,Koh kinsan mace sai da kamshi da gyara* 😉

🍀🍀🍀🍀 *Turare suna d’ayace Amma sun banbanta kowanne da ingancinsa kamshinsa da aikin sa*

🍀🍀🍀🍀 *Ina muku Albishir da UMSAD INCENSE Dan samun turaruka masu kamshi da* *gyara*

🍀🍀🍀 *Tabbas Turare sirrine ga Koh wace mace*

🍀🍀🍀 *Gamai bukatar turarukan UMSAD INCENSE*

🍀 *Na tsunguno(habil)*
🍀 *Na jiki (kwalaccam)* ( *khumra, black & white* )
🍀 *Turaren turara jiki after birth* ,
🍀 *Na d’aki(halud Al’oud)*

*UMSAD INCENSE suna kofar waika wajen Ado bayaro layout Kano State* 💃🏼💃🏼

🍀🍀🍀 *Suna bada d’aya Koh sare akan farashi Mai Rahusa*

🍀🍀🍀 *Suna bada order kayansu Gamai bukata aduk jahar da yake a fadin Nigeria*

Contact them vie
🪀08028827241 or 09033791049
IG @umsadincense

[9/27, 4:10 PM] +234 806 983 1049: 🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀
🧑‍🦯 *MATAR MAKAHO* 👨‍🦯
~ Na ~

🍃 *Rukayya* *Ibrahim* 🍃

✨Tsokaci wannan shine novel na farko Koh da za’a ga mistake Koh typing error Amin afuwa👌
free book 🤧

Back to top button